Ku Cigaba Da Amfani Da Tsaffin Kudadenku, Zamu Bi Umurnin Kotun Koli: Gwamnatin Tarayya

Ku Cigaba Da Amfani Da Tsaffin Kudadenku, Zamu Bi Umurnin Kotun Koli: Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin tarayya ta saduda game da wa’adin daina amfani da tsaffin takardun Naira da ya kamata ya zama yau Juma’a, 10 ga watan Febrairu, 2023. Gwamnatin ta bayyana cewa babu komai za ta bi umurnin kotun kolin Najeriya da ta dakatad da shirin hana mutane amfani da tsaffin kudadensu fari daga ranar 10 ga Febrairu.
Zaku tuna cewa kotun koli a ranar Laraba ta dakatad da shirin haramtawa mutane amfani da tsaffin kudinsu yau Juma’a, 10 ga Febriaru.
Ya ce dalili kuwa shine bankin CBN bai cikin wadanda aka shigar a karan, saboda haka kotun koli ba tada hurumin sauraron karar.
Ya ce za su bi umurnin kotun ne kawai saboda gwamnatin Buhari na ganin girma da mutuncin
doka. Asali: