Yan Bindiga Sun Kaiwa Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Osun Hari

Daliban kwalejin fasaha sun tabbatar yan bindigan sun kaiwa shugaban nasuhari Dr, sasom Adegoke a ranar litinin dai da tagabata
Kakin kwalejin Dr, Wale Oyekanmy shi ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da a kayi da shi osogbo, yace an kaiwa shugaban hari ne bayan wasu yan mintuna daga barinshi a ofishin sa da misalin karfe 3:20pm da yammacin ranar litinin din
Oyekanmy ya kara da cewa shugaban kwalejin dai yan bindigan sun kamasa hari ne a wata unguwa Eti-Ooni a motar shi amma hakan yacitura bayan wata mota dake daukar yashi takawo masu cikas yakuma kara da cewa sunyi harbi akan motocin nasu amma shugaban makarantar da shi da direban shi babu abunda yasame shi.
An kai rahoton lamarin wajan yan sanda lokaci da kamfanin dillancin labarai nakasa ya kuma tuntubi kakakin rundunar yan sandan na jihar SP yemisi opalola akan lamarin ya bayyana cewa suna nan sun tsaurara bincike.